Recent Updates

Silar Fyade Complete Hausa Novel

!


*🍀SILAR FYAƊE🍀*
           Free Book

          NA💋
UMMU MAHER(MISS GREEN💚

*MARUBUCIYAR*

1 UWAR GIDA NA
3 AUREN DOLE
4 RUHI ƊAYA
5 FAROUK
6 INAYATULLAH
7 ASANADIN ABAYAR SALLAH
8 AKAN AIKINA
9 JAMILA
10 DR NAWWARA PAID BOOK
11 DARASI PAID BOOK
12 SILAR FYAƊE FREE BOOK

Bismillahir Rahmanir Rahim


           1🟨2

. . . .Kuka na ke kamar raina zai fita tsabar tashin hankali,wai yau ni ce agaban gawar mahaifiyata ina kallonta bata numfashi,wani irin ihu na sake sakawa ina girgiza Ummana cikin kuka na ke ce wa"Ummana don Allah ki tashi kada ki mutu,in dai da gaske ne kin mutu to nima tabbas mutuwa zanyi".

"ke wai wacce irin mahaukaciya ce?saboda uwarki ta mutu sai ki saka mutane a gaba kina wani kukan banza?to wallahi ba a gidannan ba,banza karuwa wacce ta bawa wani ɗa namiji jikinta ya yi mata ciki,ai gashinan yanzu kin kashe uwarki da baƙin ciki kinzo kina wani kukan banza da wofi".

Da sauri na jiyo da idanuwa na da sukayi jawur kamar wuta,tsabar tashin hankalin da na ke ciki bai saka na mayarwa da Maman Nusaiba amsa ba,sai ma ba da ƙaimi da na yi akan kukan da na ke yi,don dole suka fita suka ƙyeleni sai da na yi mai isata sannan na yi shiru,ɗan ciki na naji yana ta motsi kamar zai fito wanda tun da na samu cikin baiyi motsi mai ƙarfi haka ba.
Ina ji ina gani aka fita da gawar Mamana,a duk cikin mutanen da suka zo ta'aziyya babu mai rarrashi na, ni kaɗai na ke kuka na ina share hawaye ranar yini na yi banci ba bansha ba,ƴan uwan Mama na suka kawo abinci katan katan suna ta sha'aninsu ɗaura wannan ɗaura wancen,ni dai ina ɗaki ina tunanin rayuwa ta,a shekaruna da basu wuce 15 ba naga rayuwa kala kala.

Ina ɗaki naji Baba na yana ƙwala min kira,da sauri na fito jiki na sai kakkarwa ya ke saboda rashin cin abinci ga juna biyu a jiki na.

"Ke dan iskanci shine ki ka shige ɗaki ki ka ƙwanta uban waye zai yi miki duk wannan aikin da jama'a su ke maza fito ayi da ke,banza ballagaza kawai yaja wani dogon tsaki ya fita.
Ko da na fara aikin wani irin mugun jiri ne ya dinga ɗiba na ina daurewa don nasan halin Baba yanzu zai dawo,a haka har na gama tatar ƙullin kokon,ina tuno da mahaifiya ta ina ta kuka mai ciwo.




   *             *            *

"Girke2 ake a gidan kana shigowa zaka ji ƙamshi ta ko ina,masu aikin gidan kowa da aikinsa,gida ne ƙaton gida mai ƙyau d tsari kana ganin gidan kasan gida ne na masu kuƊi sosai.

A tsakiyar garden ɗin gidan an saka wata mat ƙatuwa doguwa wacce zata sada ka da cikin gidan mai ɗauke da sunan,WELCOME MY LOVELY SON.

Hajiya Barakat ce ta ke ta zagaya gidan tana ganin irin decoration ɗin da aka yiwa gidan,wanda ya yi tace ya yi wanda baiyi ba ta ce bai yi ba.

Da wuri ta saka ƴaƴanta a gaba ƴan mata guda uku masu suna,Zeenat,Rabiat,Aisha,Fatima.

Suka tafi taro babban yayan nasu sojan sojoji wato admiral Aliyu Muhammad,A.A M.





Miss green ce💚🖊️
*🍀SILAR FYAƊE🍀*
           Free Book

          NA💋
UMMU MAHER(MISS GREEN💚)

Wattpad user name
   Rabiatu333


       5🟥6

"Me Martaba dafatan mun sameku lafiya"?.inji Salimat ta faɗi hakan tana mai sunkuyar da kanta ƙasa alamar girmamawa.

Kallonta Me Martaba ya yi yana yaba hankalin ƴarsa tilo wato Salimat,da ƙer ya buɗe balinsa irin na ƴan sarauta ya ce"lfy ƙlau gimbiya Salima."

shiru Salimat ta yi tana jin kunyar sanar da mahaifinta wannan maganar,gashi kuma babu wanda za ta faɗawa ya faɗa masa don ba ta da uwa araye yau shekarar mahaifiyarta huɗu da rasuwa.

  Yasan halin Salimat da kunya saboda haka ya janyo abin rubutu ya miƙa mata ya ce"Gimbiya a rubuta mana anan komene ne?".

cikin sanyi ta amsa ta rubuta abin cikin kunya ta miƙa masa, hannunta yana ta girgiɗi,sai da ta bawa mahaifinta me martaba sannan ta yi dana sanin miƙa masa wannan takaddar.

Mamaki sosai Me martaba ya yi,yana kallon Ƴar ta sa cikin nuna kulawa ya ce"a tashi a tafi zamu nemeki".

Jiki babu ƙwari Salimat ta tashi kamar zata yi kuka,saboda  yadda Me martaba ya yi magana don kana jin muryarsa kasan a fushi ya faɗe ta,don tasan abinda ta aikata  laifi ne babba a cikin gidan sarauta,kuma gasu fulani kun san yaren fulanj aƘwai kunya,ita dai za ta ɗauki ƙaddarar soyayya don da alama ba tada dacen masoya,ayanzu gimbiya na da shekara 25 aduniya ta ga ƙalubalen soyayya kala2 har kawo i yanzu,saboda wasu don kuɗin mahaifinta suke sonta ba don Allah ba.
***      ***        ***

Kuka sosai su afra suke kuka bayan sun dawo daga boarding skull don yanzu anyi hutu.

Ina cikin lallashinsu Khadija ta ce"wallahi Anty Rabiatu baki ƙyautawa rayuwarki ba,da ki ka bawa namiji jikinki ya yi miki ciki,yanzu gashinan kin kashe mana uwa da baƙin ciki".

  Salimat ma ta ɗora da cewa"Wallahi  Anty Rabiatu na tsaneki tsana mafi muni a rayuwata don wallahi ba zamu yafe miki ba,kin kashe mana uwarmu da baƙin cikin ki."ta faɗar hakan ta fita tana hawaye.

Afra ce kawai ta kalleni ta ce"Anty duk da a yanzu shekaru na basu wuce 15 ba amman nasan rayuwa sosai,duk da na girmi Khadija wacce a yanzu tana da sha uku da rabi 1/3,amman ta gane cewa baƙin cikinki ne ya kashe Umma, amman yana da ƙyau mu tsaya muyi miki adalci ke ma,ki faɗa mana abinda ya faru da rayuwarki don wallahi ba zamu yarda da duk wanda ya lala ta miki rayuwa ba".

ƴar dariya kaɗan Rabiatu ta yi sannan ta ce"Afra kenan kina nan da halinki na ƴan jarida?Allah dai ya cika miki wannan burin na ki".

ka saƙe Afra ta yi tana kallon yayar ta cikin tausayi ta ce"Antynmu na sanki da zurfin ciki don Allah ki faɗa min don nima in fita daga sarƙaƙiya please".ta haɗa hannayenta alamar ban haƙuri.

Riƙe hannayen Afrah na yi a hankali na ce"zan faɗa miki Afrah,don hankalinki ya ƙwanta amman a rayuwata ba na son to na asirin kowa,amman ya zama dole shima asirinsa ya tonu".

ina kaiwa nan na tashi na jingina da sip ɗin mahaifiyarmu na fara ba ta labarin.

Labarin ya ɗakko asali ne daga.. .v.




*Miss green ce*
*🍀SILAR FYAƊE🍀*
           Free Book

          NA💋
UMMU MAHER(MISS GREEN💚

Wattpad user name
   Rabiatu33

       3🟩4

. . . . .Cikin ta kunsa mai kyau da tsari ya fara sakkowa a jirgin ,fari ne ƙal kamar zaka taɓa sa kaga jini tsabar farinsa,yana da jiki da kuma tsayi, ƙyaƙƙyawa ne shi ajin  farko,yana sanye cikin wasu haɗaɗɗun ƙana nan kaya,waɗanda suka amsa sunansu ya cire cort ɗinsa ya riƙe a hannu yana gƴara necktail ɗinsa.

Ayshe ta fara hangosa ta ce"Hajiya ga yaya cen yana sakkowa,gaskiya yaya ya daɗa ƙyau wallahi gaskiya Hajiya yaya ya fimu Ƙyau".

   Rabiatu ta ce"ke kuma kina kishi ko?ke dai wallahi aisha kishi ne da ke wallahi,ke ce ki ka yo dangin Papa shuwa arab kishi ne dasu".

Hajiya ta ce"kuyi wa mutane shiru zaku fara halin ko?".suka ja bakinsu suka yi shiru ita daman Zeenat da Fatima miskilanci ne dasu irin Yayansu.

Zeenat tana da shekara 25,sai Fatima 22,sai Rabiatu shekara 19,sai Fatima auta mai shekara 17.

shi kuma babban gogan yana da shekara 35 a duniya,Har hajiya ta fitar da ran haihuwa sai kuma ta dawo ta haifi mata har huɗu.
Da sauri Hajiya ta ƙarasa ta rungume ɗanta cikin so da ƙaunarsa duk da sojojin da ke bayansa,shi kuwa jan zaki Aliyu Haidar kunya ce dashi sosai,don haka cikin kunya ya rungume ta,shi daman tun yana yaro kunya ce dashi,tun yana shekara 4 ya daina yadda mahaifiyarsa na yi masa wanka,sai dai ya rufe gabansa ta yi masa,haka har ya girma shi mai kunya ne.

Yana cikin cin abinci wayarsa ta kama ringing ɗin wayarsa,ya ƙi ɗauka Hajiya Barakat ta ce"haba son ka ɗauki wayar mana kaji ko menene?".ta faɗi hakan cikin yaran yarbanci,shima cikin yaran ya ce "to momi".

"Haba A/D ka tausayamin ka dinga ɗaga waya ta,kasan dai babu ƙyau wulaƙanta ɗan adam, please ka yadda ina sonka tsakani da Allah".

"oky".

   kawai ya ce mata ya kashe wayar.

Salimat ta goge hawayen da suka zubo mata don matuƙar ba ta auri admiral ba komai zai iya faruwa,ya zamar mata dole Ƙara Ƙaimi wajen yin addu'ah don komai yazo da sauƙi,tana cikin wannan tunanin ta tashi ta shiga bathroom ta ɗauro alwala ta fara yin sallah tana kai kukanta ga mahaliccinmu subhanahu wata ala.





  ***       ***      ***

yau aka yi 7 ɗin mahaifiyata dangi duk sun fara tafiya,har yanzu mutuwar mahaifiyata tana cikin ƙoƙon zuciyata,na share wata ƙwallar da ta cukomin ƙwarmin idanuna,na gogesu ina cigaba da ƙara tsanar wannan bawan Allahn da ya yi sanadin rugujewar rayuwar a halin gidanmu.

Ƙannena uku ne duk suna bording skull,Salimat,Afra,khadija.

Har lokacin kuma ba a gaya musu rasuwar mahaifiyarmu ba,ko ya ya zasuji idan suka ji mahaifiyarmu ta cika oho?.

ina cikin wannan tunanin naji an watsomin ruwan kanzo mai sanyi,don alokacin safiya ce,na waiga don ganin maiyi min wannan izayar,mmn nusaiba ce da kuma Hafsatu,wacce ta  kasance ƙanwa awajen mahaifina.

Suna ta kumfar baki wai na iya munafunci na shiga ɗaki na ƙi fitowa don nasan na yi abin kunya.

Wasu hawaye ne masu zafi suka fara fitomin a ƙwarmin idanuwa na,na gogesu na fita don yin aikin da suka ce zuciyata tana yimin ƙuna.





*miss green ce*
*🍀SILAR FYAƊE🍀*
           Free Book

          NA💋
UMMU MAHER(MISS GREEN💚)

Wattpad user name
   Rabiatu333



             7🟦8

"Wata rana Umma ta aiki ni gidan Baba Na sidi sai akai rashin sa a ranar anyi ruwa kamar da bakin Ƙwarya,har Mama Khaltum tace in ƙwana na ce mata ai ban tambayi Mama ba,babu yadda bata yi dani ba nace ni tafiya zanyi haka na biyo hanya ga dare ga komai haka na fito ina ta tsare motoci amman babu wacce ta tsaya.

  Na yi tagumi kamar zanyi kuka wata ƙyaƙyawar mota ce naga ta shawo ƙwanar titin,banji tsoro ba haka na tashi naje tsakiyar titi,ina tsayar da motar da hannuna,baiyi niyyar tsayawa ba amman sai da na tsayar dashi,sauke glass ɗin ya yi,kansa a ƙasa bai kalleni ba ya ce"come in".

da sauri na shiga ina ta raba idanuwa,ban kalli mai motar ba shima bai kalleni ba,da alama bashi da lafiya don naji yana ta numfarfashi ni kuwa tsoro na ya ƙara ƙaruwa sosai jin wani baƙon al'amari yana ta ziyarta ta,shima a nashi ɓangaren haka wannan abin ya dinga faruwa.

In ta ƙaice miki a wannan dare ne abubuwa da dama suka dinga faruwa,na samu kaina a mai ƙin hanashi duk abinda ya ke son faruwa,tun abin yana tafiya gentle gentle har dai ya yi tsanani,ban san me ya faru dani ba?ban taɓa jin tsananin feelings ba sai aranar,a wannan dare komai ya faru kuka na ya tsananta sosai.

  Shima hankalinsa ya tashi sosai da sosai,don ina jin gunjin kukan da ya ke yana cewa Allah ka sani ban taɓa zina ba,ban taɓa kusantar ta ba sai yau ya Allah idan mafarki na ke ka farkar dani ya Allah.

A matuƙar hargitse na fito daga cikin motar ina ji yana ta yimin magana don shima har fitowa ya yi,amman na fizge hannunsa na tsayar da wata adaidaita kamar ƴan party ya ɗebo,akayi sa a unguwarmu ɗaya don haka muka tafi.

Ina dawowa Baba yana kiciniyar kulle gida don sun san tunda na kai yanzu to sai gobe zan dawo,mamaki Baba ya yi na ganina amman bai ce komai ba ya matsamin na wuce,kai tsaye ban ɗaki na wuce ina kuka haka na cire sutura ta,kamar a mafarki haka na ke ganin komai yana dawomin,to me ya faru dani haka na bada kaina ga wani wanin ma ban sanshi ba.

Kaca kaca siket ɗina ya yi da jini ina kallonsa na saka wani ihu a banɗaki,Baba da ya ke a tsakar gida hankalinsa ya tashi yana tambaya ta lafiya,shiru na yi ina rufe baki nan ina kuka don tabbas na cigaba da kukan to kaina xan tonawa asiri.

Don wannan abin ba dole ya yi min ba,ban san me ya shiga brain ɗina ba,Rabiatu me addini me kishin musulunci,me girman kai awajen wasu saboda kamun kai to me ya sakani aikata haka kuma?.

Ina fitowa ina ɗingishi na hango Baba da Mama suna tsaye cirko2  suna kallo na na sunkuyar da kaina zan shige ɗaki,Mama ta daka min tsawa ta ce"aiken ne sai yanzu?Kuma me ya samu ƙafarki ki ke ɗingishi"?.

wani mummunan faɗuwar gaba ne ya riskeni,gaba na yana dukan uku uku na buɗe bakina daƙer na ce faɗuwa na yi Mama,ba tare da ta ƙara cewa koma ba ta shiga ɗaki ita da Baba.cen kuma ta fito a lokacin ina zaune na yi tagumi da hannu bibbiyu ga ƙasa na kamar zai tsage saboda tsananin zafi.

"Rabiatu ina saƙo na"?.

sai alokacin na hau dube dube don sai yanzu na tuno na barshi a motar wannan azzalumin mutumin.



Anan zan tsaya saboda matsalar chagi.


*Miss green ce🍀*
*🍀SILAR FYAƊE🍀*
           Free Book

          NA💋
UMMU MAHER(MISS GREEN💚)

Wattpad user name
   Rabiatu333

 

       9🟫10

. . .. .kuka na fara yi wa Mama ina bata haƙuri,cikin faɗa ta ce"to yanzu ina saƙo na ki ka fara kuka?ko dukanki na yi?",cikin kukan na ce"wallahi Mama saƙon ya faɗi ki yi haƙuri don Allah".

ta fa hannu ta fara yi tana salati ta ce"yanzu Rabi'a yarmin da kuɗin adashin ki ka yi kuɗi dubu hamsin da ɗoriya?amman kin cuce ni Rabi'a yanzu me zance da masu bina bashi"?.

Har yanzu kuka na ke Baba na ya shigo ya ce wa Mama ta yi haƙuri idan ya ɗauki salary zai bata dubu talatin ta rage asara.

Da safe da ƙer na tashi na tafi makaranta gashi muna jarrabawar waec da Neco munyi waec saura Neco,ban rubuta wani abin azo a gani ba,shiru kawai na yi dana shiga ɗakin exam ɗin,na yi ta gumi ina tunanin rayuwa ta,yanzu shikkenan wani cen ya ɓatar min da tantanin budurci na?me zance wa mijin da zan aura?alokaci ɗaya na tuno da Salis gumi ya shiga tsatstsafomin,don tuno da yadda ya ke ƙwatantamin daren farkonmu,to ni ta ina zan nishaɗantar dashi alhali kuma ina on-virgin.

Dukan tebir ɗin dana ke kai wani invigilator ya yi sannan ya ce"lfy me ya faru?can i help u?".

duk lokaci ɗaya ya yi min wannan tambayar yana yimin wani irin kallo,sai a sannan na gane shi malamin daya na ce min sosai kamar wani cingum,na ɗanyi tsaki kaɗan yadda ba zai ji ba,na turo ɗan ƙaramin baki na gwanin sha'awa.
   Lumshe idanu jibril ya yi yana tasbihi a cikin zuciyarsa,don matuƙar ya kalli Rabi'at yana tsintar kansa a cikin wani hali ya juya yana kallonta sosai yarinya kyakkyawa da ita,wato Rabi'at ita ba doguwa ba ita ba gajeriya ba,tsaka tsakiya ta ke,tana da yalwar mazaunai sosai don shiyyasa ma bata saka mayafi kullum sai hijabi,choco colour ce tana da siririn hanci da ɗan ƙaramin bakinta dai dai gwargwado,tana da idanuwa masha Allah waɗanda suka yalwatu da siraran eyelashes masu ɗaukar hankali,pinck lips ɗinta mai matuƙar ɗaukar hankali,tana da gashin jiki wanda ya ƙwanta luf gwanin sha'awa.

To wannan kenan.

Tunda wannan abu ya faru a rayuwata sai na zama so silent wani lokacin sai dai in shiga ɗaki inyi kuka in share hawaye na,abin dai yana matuƙar damuna,Mama tayi2 in faɗa mata abinda ya ke da muna amman abu ya gagara.

Cikin wannan halin ne na yi wani irin fari sosai na ɗashe sosai idanuna sukayi fari ƙal kamar madara,mama na suka ciko sukayi Ɓam dasu,tun abin baya damun mama har ya fara damunta ta shiga bincika ta don yadda na ke matuƘar Ƙellin goshi abin sai wanda ya gani,daman mazaunai ba a maganar su.

On serious Mama ta kafe ni da idanu ta ce"Rabi'atu yaushe rabonki da period?".

Wani irin faɗuwar gaba na ji idanuwa suka kawo ruwa daman ina da matuƙar saurin hawaye,Mama ta daka min tsawa ta ce"me ya faru da ke Rabia na shiga uku me zan gani a gidana?Rabia cikin shege a gidana,mari ta kaimin na kauce ina kuka Baba ya shigo don tambayar ba asi Mama ta hau nu na ni kamar ta ga abin tsoro.

"Ke me ki ka yi mata ta ke nuna ki"?.

ya faɗi hakan cikin tsawa da sauri na ce wai banyi period ba?,gumi ne ya fara tsastsafowa Baba ya ce"Maryam ki faɗa min gaskiya me ya faru da ƴarmu,cikin kuka Mama ta fara faɗa mai duk sauyin dana ke samu,Abba na ya katseta da cewa ta shi mu tafi asibiti zaman gida bai ka ma mu ba.

Test ɗin farko ya nuna ina da shigar ciki har na tsawan wata biyu.

Tun daga wannan ranar Mama ta faɗi jininta ya yi mummunan hawa sosai tun daga nan komai ya canza a gidanmu,idan ka shigo kamad gidan ma ko ki,daman daga ni sai Mama tunda su Afra suna makarantar boarding,yin duniya an tambayeni wanda ya yimin ciki amman naƙi ba da amsa sai kuka har suka gaji suka saka min idanu,ga shi cikin kamar ba na fari ba,don yadda ya ke da matuƙar girma na zama wata babbar mace ko ina ya ciko.

Tun daga ranar da Abba yasan ina da ciki ya daina yimin magana musamman da matarsa ta kamu da ciwo akaina don yana mayuƙar son Mama don yadda kasan layla majno haka suke.sannan Abba ya kori Salis bayan shima yasha tuhuma daga mahaifina don Abba na ƙin yarda ya yi shine ya yi min ciki don yadda muka shaƴu sosai dashi.

Tun daga nan Mama ta yi ta ciwo da ya ke ciwon ba na tashi bane Mama ta mutu,kuka sosai Rabiatu ta farayi don tunowa da mahaifiyarta Afra tana taya ta kukan haka sukayi ta yi babu mai taya su har sukayi shiru.

Cikin kuka Rabiatu tace"wannan shine gaskiyar labarin Afrah,a ina zanga wannan bawan Allah wanda rana ɗaya ya lala tamin rayuwa?da ma ace na ganshi yanzu".sai ta fashe da kuka sosai ya yinda ɗan cikinta ya ke ta wutsil2 babu abinda ya shafe sa.



*Miss green ce*
*🍀SILAR FYAƊE🍀*
           Free Book

          NA💋
UMMU MAHER(MISS GREEN💚)

Wattpad user name
   Rabiatu333

Arewabooks
rabiattu0444




     11🟦12

. . . .haka muka yi ta kukanmu babu mai rarrashin mu tun daga ranar babu wanda ya Ƙara kukani,Salimat da khadija ko kallon inda na ke ba sayi,Afra ce kawai ke kulani don dama hutun sallah suka zo.



*Bayan wata uku 3*

    Rannan ina ƙwance naji wani mugun ciwo baya ya kamani ga ciwon mara me tsanani ni kaɗai a cikin ɗaki ina ta kiran sunan Allah gwanin ban tausayi abin sai wanda ya gani,na haɗa wata uwar zufa sannu a hankali gumi ya ringa tsattsafomin ɗan cikina ya koma ƙasa baki ɗaya yana ta motsi kamar zai fito.
  Afrah ta shigo kawomin abincin safe taga halin da nake ciki,da sauri ta je ta kirawo su Khadija sai da suka zo buɗe bakin Salimat ta ce"wallahi da ina da dama da sai na kashe Wannan cikin harda uwar ma,don sun jawo mana raini da cin fuska da zagi a gari,ta juya ta kalli Khadija ta ce to ni dai na tafi wajen Asil birthday ɗinshi idan kinga dama ki zauna wajen wannan akuyar idan kin ga dama ki taimake ta".
  tana faɗar hakan ta saka kanta gaba ta yi tafiyarta.

Khadija ma tafiyarta ta yi tana surutai,Afrah ta kalleni cikin tausayi ta ce"Anty jikin da sauƙi yanzu ko in aika akira abba a majalisa".

  Da sauri na girgiza mata hannu alamar kada ta kirasa,ni dai kawai kiran sunan Allah na ke asannu ,a sannu kan ɗa ya fara fitowa na ƙwanta a kan gado ba buɗe ƙafafuna Afra ta riƙe hannuna tana zubar da hawaye,kanta a sunkuye don ba ta son ganin tsiraicina,a haka na dinga faɗin sunan Allah har ɗa ya fito kyakkyawan yaro fari ƙal kamar ɗan larabawa.
Da gudu Afrah ta fita tana haɗa hanya ta shiga gidan Mmn Nusaiba don ta faɗa mata,ta kalli Afrah sheƙeƙe ta ce oh yau Allah ya yi an haifi shege ni da ina da iko da sai na kashe shegen banza".
  Tana faɗin hakan ta yi shigewarta ɗaki tana ta surutai.

  Har ta fito daga gidan ta hango mmn junior kishiyar Maman Nusaiba,ta ce"a ah lfy Afrah me ya farunne?".kunsan maganar gwarawa.

Nan Afrah ta faɗa mata a taƙaice,da sauri Mmn junior ta faɗa gidan tun kafin Afrah ta ƙarasa faɗa mata.

Tana shiga ɗakin ta jiyo nishin Rabiatu da sauri ta ƙarasa ciro mata ƴar budurw Ƙyaƙƙyawar gaske,wani gauran numfashi Rabiatu ta saki tana kiran sunan Allah.

Yaran mmn junior ta fara gyarawa tsaf,sai dai babu kayan saka musu da sauri ta tafi gida ta ɗebo kayan da ta fara tarawa saboda haihuwar da za tayi watan gobe, kala biyar ta ɗebo masu kyau ta sakawa yaran sukayi ƙyau  gwanin sha'awa.

Sannan ta gyara Rabiatu tsaf ta gasata da ruwan zafi sannan ta riƙo ta kamar ƙaramar yarinya,ta saka Afrah ta dafa min ruwan tea da harda madarar ƴan boarding su Afrah.

wani kuka ne yazo min tuna maraici,idan banda maraici me zaisa har mace ta haihuwa a rasa me gyarata,duk da cikin shege ne amman da mahaifiyarta tana nan duk Ƙin da ta ke yiwa yaran za ta kulasu.

Asannan na tuno da AUNTY Rabiatu ƙanwar mahaifiyata wacce ta ke a merica da mijinta,wacce har yanzu bata san yayarta ta rasu ba,saboda sanin irin halin da zata shiga.
***          ***         ***

wani mummunan faɗuwar gaba yaji a take ya zauna yana faɗin sunan Allah messenger ɗinsa ya shigo kawo mai saƙo,da hannu ya nuna mai ya ajje ya tafi,messenger ɗin ya kalli ogan nasa amman babu damar magana saboda halin da ya tsinci kansa alokaci ɗaya,ya shiga kiran sunan Allah har dai abin ya tsagaita masa,amman ranar babu damar aiki don haka ya nufi gida,don har yanzu zuciyarsa zafi ta ke masa.


  ***    ***      ****

"Aliyu abinda ka ke ka yi gaggawar zuwa gida ina son yin magana da kai".

"oky hjy gani nan zuwa".

Hajiya Barakat ta zauna a ɗaki tana jiran zuwan Aliyu,Fatima tace"Hajiya kada ki faɗawa Bro wannan maganar ransa zai ɓaci wallahi".cikin yaren yaroba ta faɗi hakan.

Hajiya Barakat ta daka mata harara ta cigaba da danna wayarta.



*Miss green ce*
https://arewabooks.com/chapter?id=62966a04b3924a9ab448be72


*🍀SILAR FYEƊE🍀*

NA💋
UMMU MAHER(MISS GREEN💚)

Wattpad user name
   Rabiatu333

Arewabooks
rabiattu0444

13🟪14

"Aliyu da ma jiya munyi magana da alajaa Hajara kan  maganar aurenka da Ƴar wajenta Rasheeda shiyyasa na ce bari in faƊa maka idan yaso Sai Kaje ka ganta ku haƊa kanku."

Tunda ta fara magana Aliyu yaji ransa lokaci Ɗaya ya tashi,a halin da ya ke ciki yanzu na busy shi bai ga abinda zaiyi da wata mace ba,kai idan ma ya ce zai auren ai cutar matar zaiyi,kuma bayan haka ko da auren ma zaiyi zai auri mace mai kunya ne ba Rasheeda mara kunya ba,yana cikin tunanin ya jiyo Hajiya na cewa"ka tashi ka tafi Allah ya yi maka albarka na ji da Ɗin wannan biyayyar da ka yi min kai ma Allah ya baka masu yi maka".

shi dai admiral A.rasa me zai ce ya yi ya tashi ya tafi kansa na mai tsananin sara masa,ya shiga ban Ɗaki ya sakarwa jikinsa ruwa.

ya rasa me yasa ba ya son ko zancen aure?ya rasa abinda yasa kuma baya jin feeling a duk macen da ya kusanta,bai taɓa kuma son wata ɗiya mace ba tunda ya ke a rayuwarsa har kawo i yanzu da shekarunsa sun dushi 37.
***

Wani irin hamdala gimbiya Salimat ta yi sannan ta ce"ranka ya daɗe ina mai miƙa godiya ta a gareka abisa son dukkanin farin ciki na matuƙar alkhairi ne sai ka tabbatar da ka sama min farin ciki na."

Ƴar fara'a nahaifin Salimat  ya yi sannan ya ce"babu komai gimbiyar mata,ai abinda ki ka zo dashi ba abune wanda ya zama sabo ba,sunnah ce ki ke son yi don haka ina miki fatan alkhairi aduk inda ki ke gimbiya.

Cikin jin kunyar mahaifin na ta,ta tashi ta shige sashinta tana ji a zuciyarta kamar ta samu Admiral A. Ta samu.

Shu kuwa gogan Admiral A.ba ƙaramin kaɗuwa ya yi ba da ganin Mai martaba har cikin office ɗinsa,kuma ya nemi yardarsa wajen auren ƴarsa,kunya da kawaici  sosai Admiral A. Yaji don haka cikin nutsuwa ya amsa masa zai auri Salimat ba bisa tursasawa ba,a zuciyarsa kuma yana mamakin irin mugun son da Mai martaba ya ke yiwa ƴarsa Salimat,mai makon namiji yaje neman aure amman sai aka ɓige da nemawa ƴa.

Kan Aliyu gaba ki ɗaya ya kulle ya rasa me zaiyi taka mai mai ga Hajiya ta saka shi a gaba akan Rasheeda,ga Mai martaba shima da ya sako shi a gaba akan Salimat kuma Mai martaban ya ce baya son bikin ya wuce wata ɗaya,haka zalika itama Hajiya ta ce ba ta son ya wuce wata 1.

to wa zai aura a cikinsu yabar wata?ana nufin sai dai ya haɗa su rana ɗaya ne ko kuwa?shi kansa gaba ki ɗaya ya kulle gashi yanzu wani irin tulo masa aiki a keyi a office.Ga ba ki ɗaya kansa ya yi mugun kullewa.





***

A hankali na ke rainon ƴan biyu na,kyawawa dasu kamar ka sacesu ka gudu saboda tsabar ƙyau da ƙwarjininsu,Abba na kuwa kullum cikin hantara ta ya ke yi dani da ƴan biyu na,ko laifin me su kuma sukayi oho.

Daman bai taɓa ɗaukarsu tun suna tsummansu har yanzu da suke wajen wata na uku.

Mmn junior ita ke kula da komai nawa hatta wankan jarirai ita ce ta yi min har nima kaina ita ta yi min,kaya kuwa kullum cikin aiko min dasu ta ke masu kyau.

Dangin Abba na dana Mama na babu wanda yazo don ya dubani ko yaga halin da na ke ciki.


Busy🤯

*Miss green ce*
https://arewabooks.com/chapter?id=6297ab36c8d26a9288bb4632

.*🍀SILAR FYAƊE🍀*

NA💋
*UMMU MAHER(MISS GREEN💚)*

Wattpad user name
   Rabiatu333

Arewabooks
rabiattu0444

15🟩16

Rana ba ta ƙarya sai dai uwar ɗiya taji kunya,yau saura sati guda auren Admiral A.da zanka zankaɗan matansa Salimat da kuma Rasheeda.

A ɓangaren ango dai babu wani shiri da ya ke,tunda aka fara shirin bikinma sai yau ya dawo daga tafiyarsa zuwa Holland,ya fito daga banɗaki kenan daga shi sai boxer yana goge jikinsa da tawul ɗin daya riƙo a hannunsa,gashin jikinsa ya ƙwanta luf luf,kawai ji ya yi an buɗe ɗakinsa an shigo babu ko sallama,da sauri ya juyo don ganin me yi masa wannan aika aikar don ya tabbata Hajiya ba za ta taɓa yi masa haka ba,su ma su Fatima ba za suyi haka ba don suna matuƙar jin tsoronsa.

Rasheeda ya gani a tsaye akansa kamar wata doki,babu tsayuwa ma irin ta mata a ah yadda kasan namiji haka ta ke,bata iya action irin na mata ba.

Wani banzan kallo ya yi mata sannan ya ce"ke! lfy zaki Shigo min ɗaki ba tare da sallama ba,haka aka koya miki rashin respect".

ya faɗi hakan ya haɗe girar sama da ta ƙasa gashi ƴar wannan maganar da ya yi har ya fara haki don bai saba doguwar magana ba.

"Ai daman dole ka tambayeni me ya faru?ashe daman kai macuci ne maci amana,daman ba ni kaɗai zaka aura ba,to wallahi baka isa ka haɗa ni da kowacce mace ba don ni kaɗai aka halicce ka,don duk macen da ta raɓe ka ta raɓi mutuwarta".

Kallonta kawai Admiral ya ke yana mamakin tsiwa da rashin tarbiyya irin na Rasheeda,ya rasa me ma zai ce mata duk shiru shirunsa ya ga alamar Rasheeda ƴar zafin kai ce kawai so take ta ɗora mai hawan jini.
Wata uwar tsawa ya daka mata sannan ya nuna mata hanyar fita ba tare da ya kalleta ba,da gudu ta arta ana kare gabanta yana mugun faɗuwa don ba ƙaramar dauriya ta yi wajen tsayawa ta yi mishi wannan tsiwar ba,tana fita ya riƙe kansa da ya ke sara masa don  matuƙar ya yi magana da ƙarfi sai yaji kansa yana masa ciwo.

Da kuka ta samu Hajiya tana faɗa mata wai Aliyu ya zage ta,kallonta Hajiya Batakat ta yi sannan ta ce"ke fa Rasheeda ba ƙya bin komai a hankali,na gaya miki halin Aliyu yana da zuciya kuma mutunne mara son haya niya,kinga kuwa dole idan kina son kama mijinki a hannu sai kin iya makirci da sauransu sannan zaki mallekishi,kuma ko baki da haƙuri sai kin koya don Aliyu yana matuƙar son mai haƙuri,kinga wannan yarinyar ƴar sarkinnan tana da matuƙar haƙuri sosai shiyyasa har Aliyu ya yadda da aurenta saboda haƙurinta da kawar da kai,don haka kema ya kamata ki zama mai haƙuri sai kiga kin zama tauraruwa."

Mahaifin Aliyu Shima haka ya ke da zuciya Allah yajiƙansa da rahama.

to da wannan shawarwarin yasa Rasheeda yin shiru sannan tana ayyana wa acikin zuciyarta ko ta halin ƙa-ƙa sai ta zama sarauniya a idon Aliyu.

Kuɗi sosai Aliyu ya ware ya bawa Hajiya Barakat na kayan lefe,da kanta taje dubai da wata ƙawarta suka siyo kayan lefe na gani na faɗa,ko wacce a cikinsu dozin biyu aka yi mata masu ƙyau da tsari,amman ba kala ɗaya bane don sai da aka tambayi kowaccensu ta faɗi kalar da take so.

Dinner kala biyu aka shirya ta farko Salimat ce ta shirya kayarta,a wani babban hall wanda ya gaji da haɗuwa,da ƙer Aliyu yaje don har kuka Salimat sai da tayi rannan sannan yazo sunyi matuƙar ƙyau,kayan da suka saka white ne ita ta saka gown fara ƙal sai net mai ɗaukar hankali,shi kuwa gogan farar shadda ya saka wacce taji aiki tana ɗaukar ido.

Ranar hauka ne kawai Rasheeda ba ta yi ba,saboda yadda wajen partyn ya haɗu sosai sannan su fatima duk sunje,ƙannen ango da amarya sun saka skye blue ɗin gown wadda ta yi matuƙar yi musu ƙyau.

Ana ta watsa musu sky ɗin rose flowers,abin sai wanda ya gani,hatta cake ɗin su ma sky ne.
  

  Rasheeda ma ta yi na ta Dinner ɗin sai dai ko kusa bai kai na Salimat ba,Kuma gashi babu ango don tafiya ta tasowa Aliyu zuwa Germany don haka ya yi tafiyarsa don gaba ki ɗaya Nigeria ɗin ta ishe sa.
Ƙarshe har aka ɗaura aure baya nan don yana sane ya damƙa komai a hannun Amininsa Sooraj har haɗaɗɗen gidan da zai zauna da ke Abuja huse road,mai part huɗu wanda ya gaji da haɗuwa.

Haka nan aka fara ɗaura auren Salimat sannan na Rasheeda,wanda hakan ba ƙaramin baƙanta ran Rasheeda ya yi ba har ma da Hajiya Barakat ta ji haushi,sai dai ba tada bakin magana don ƴan uwan mahaifin Aliyu ne suka tsara komai,don mahaifinsu Aliyu Bafula tani ne shi,kun san Fulani kuma da haɗin kai.
***    ***    ****

Rabiatu tana ƙwance tana yiwa Afrah wanka ƴan biyunta kenan don Ammar da Afrah sunan yaran,hannunta har kakkarwa ya ke saboda wata muguwar yunwar da ta ke ji,a yanzu Ƙanwarta Afra ta koma makaranta,Khadija da Salimat ne a gida saboda sun zana jarrabawar waec da neco shiyyasa ma basu koma ba.

Ƙwata2 sun daina bawa Rabiatu abinci tana ji tana gani suke rabewa tsakaninsu su cinye,sai dai idan sun bar ɗan ƙanzo ta tattare taci a haka.

Don ma ƴan biyu suna da kufan jiki don ko a yanzu yadda kasan wasu ƴaƴan commisioner haka suke.

Bani da mai taya ni hira idan ba ƴan biyu na ba,sai Mmn junior amman su Salimat ko kallon inda na ke ba sa yi.

Wani lokacin idan na kalli Twins sai na fashe da kuka idan suka girma suka tambayeni ina mahaifinsu me zance musu?sai wani kuka yaci ƙarfi na yaci ƙarfina in ɗaga hannuna sama ina kuka ina roƙon Allah ya ya buɗe min wannan lulluɓin zanin in gane waye ubansu Afrah.

Ina cikin wannan tunanin naji gidan ana ta koke koke ban san ko meye ba,jiki na yana rawa na fito tsakar gidan don jirin da na keji,Afrah tana ta kuka don cire mata Mama da na yi a bakinta.


*Miss green ce*
*🍀SILAR FYAƊE🍀*

NA💋
*UMMU MAHER(MISS GREEN💚)*

Wattpad user name
   Rabiatu333

Arewabooks
rabiattu0444



17🟨18

Wani tsalle na yi na rungume Anty Rabi ƙanwar mahaifiyata wacce naci sunanta,kuka sosai mukayi a ranar tuno da Mama,sannan Anty Rabi ta ce"babu abinda ban sani ba taƙwara na sanki tun kina ƙaramarki nasan abinda zaki aikata nasan wanda ba zaki aikata ba,amman ina mamakin yadda hakan ta faru".

Kuka ne ya ɓalle min ina cewa"Anty Rabi wallahi ba laifina bane ban san sanda abinnan ya faru ba,na rasa yadda zan fassara abin,na rasa wa zai bani shawara".sai na fashe da wani irin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro.

Wani kallon rainin hankali su Khadija suke min don gani suke kawai raina wa mutane wayo na ke amman nasan komai,a ganinsu ta ya ya mace za tayi cikin shege sannan wai ta ce bata san wanda ya yi mata ba?.

A hankali na bawa Anty Rabi labarin komai ina kuka kamar raina zai fita.

Shiru ta yi tana ɗan nazari na sannan ta ce"babu komai Rabi atu Allah n daya ɗora miki shine zai warware komai da yardarsa,abinda na keso da ke ki cire wannan tunanin a ranki ki cigaba da addu'ah Allah ya bayyana komai".

Ƙwananta ɗaya ta ce za taje rijiyar zaki gidan kakaninmu sannan za ta dawo mu tafi Abuja tare da ita don zamana anan ba zai yiyu ba.

naji daɗi ta wani ɓangaren don nasan can babu mai zagi na ballan tana hantara,kuma ga su Laila ƴarta kusan sa a ta ce nasan zan samu nutsuwa.

Amman idan na tuno da barin gidanmu sai naji wani kuka ya kufcemin,ina tuno irin rayuwar da su Salimat zasuyi,don tun yanzu Salimat idan ta fita tun safe sai yamma ta ke dawowa,don tun safe idan Abbanmu ya fita sai dare ya ke dawowa,babu yadda ba ayi da Abbanmu ba akan ya yi aure amman ya yi banza da al'amarin.
da wuri na haɗa kaya na,na shirya twins cikin kayan sanyinsu wanda ya ƙarɓesu sosai gwanin sha'awa ɗaya daga cikin wanda Anty Rabi ta kawo mana jiya da tazo.

Har gida naje na yiwa Mmn junior Sallama tana ta kuka,Mmn nusaiba kuwa cewa ta yi Allah ya raka ta ki gona,daga nan ma in huce birnin sin.

Da wuri Anty Rabi ta dawo alokacin Abbanmu yana shirin fita ta ke sanar dashi hukuncin da ta yanke,magana ɗaya ya faɗa wacce sai da na zubar da hawaye ya ce"Allah ya tsare hanya idan taje ma kada ta ƙara tunawa cewa ni ne ubanta".

abin y ƙular da Anty Rabi sosai amman ba tace komai ba har ya tafi,su kuwa ƙannena su Khadija kallona kawai suke yi amman sun kasa cewa komai har muka rabu.

Idanuwa suna zubar da ƙwallar rabuwa da gida shekara 17 kenan da aka haifeni a wannan gida ban taɓa ƙwana awani waje ba idan ba gidanmu ba tunda ba a saba mana da ƙwanan wani waje ba,ko da kuwa Rijiyar zaki ne unguwar iyayen su Mamanmu.

Tun da na ke a rayuwata yau ne rana ta farko dana hau jirgi sai tsoro ya kamani Anty Rabi ta amshi Ammar ni kuma ina riƙe da Afrah.

Cikin lokaci ƙanƙani muka sauka A Abuja,masha Allah kawai na ke faɗa saboda yadda garin ya ke gwanin sha'awa ga shi luf luf da ya ke lokacin sanyi ne.

Ban ƙara mamaki ba sai da muka shigo unguwarsu Anty Rabi ko wani gida da sunan mai gidan,duk gidan da ka gani sai ka ƙara kallonshi saboda ƙyau da tsaruwarsa.

Gidansu Anty Rabi ma gida ne mai ƙyau ga shi ƙato gwanin sha'awa sanyi da Ƙanshin flowers suna ta yi maka barka da zuwa,ji na yi kawai an rungume ni Laila na gani a gaba na tana ta dariya ta amshi Afrah a hannuna ni kuwa sai kallonta na ke yadda ta ƙara fari ƙal ga wata uwar ƙiba da ta yi,acikin lokaci ɗaya na tuno da yadda na ke ada.
***      ***    ****

Motoci ne sun kai goma suka shigo ƙyaƙyawar unguwar a cikin ta tsakiya ne na hango Admiral A.yana zaune da system ɗinsa a hannu,yana ɗan wani nazari bisa wani bincike da ya ke.

Wayar sa ce ta ɗauki ƙara ganin mai kiran ya sa ya ɗauka a hankali,cikin girmamawa ya ke gaishe da mahaifiyar ta sa cikin yaren yoruba.

Ta ke tambayarsa ya iso Nigeria ne? ya ce mata eh ya shigo?nan ta ƙara yi masa nasiha akan ya kula da matansa musamman ma Rasheeda don ita ce ƴar uwarsa,to kawai ya ce mata sannan sukayi sallama.

A cen ɓangaren su Rasheeda da kuma Salimat kowaccensu taci ƙwalliya ta alfarma don taron miji musamman ma da yau suka cika ƙwana biyar a ɗakinsa ba tare da sun saka shi a idanuwansu ba.





*Ummu Maher ce*
*🍀SILAR FYAƊE🍀*

NA💋
*UMMU MAHER(MISS GREEN💚)*

Wattpad user name
   Rabiatu333

Arewabooks
rabiattu0444

19⬜20

Kai tsaye ɓangarensa ya nufa bai nemi kowaccensu ba,Rasheeda kuwa ta kafa ta tsare tana jikin windon ɗakinta ta saman bene tana hango Admiral A.sanda ya shigo don haka har komawa ɗaki ta yi ta ƙara shafa hoda da janbaki tare da ɗakko wani turarenta mai mugun ƙarfi ta shafa.

Ita kuwa Gimbiya Salimat tana kan sallaya ta ɗaga hannuwanta biyu tana roƙon Allah akan Allah ya mallaka mata ziciyar Sojanta.

Tana cikin wannan addu'ar jakadiyarta ta shigo tana neman iso,tana shigowa ta ce"uwar ɗaki na kuma uwar gida a wajen angonta Admiral A.Yanzu naga motocin Admiral sun shigo gidannan, don haka na garzayo don inzo in gaya miki wannan albishir.
Ɗan murmushi Salimat ta yi sannan ta ce"nima ina yi mishi barka da dawowa Allah ya tsare mana shi a duk inda ya saka ƙafafunsa,amman bazan je ɓangarensa ba don a yanzu hutu ya ke buƙata don haka nasan da kansa zaizo".

kallonta Jakadiyarta ta yi sannan ta ce"haba uwar gijiyata kin fa san ba ke kaɗai ce matarsa ba yana da wata,ba kya tsoron ita yanzu taje ke baki je ba."

"Hmm Yaya na fuskanci abinda ki ke nufi amman nasan kinfi kowa sanin ƴaƴan sarauta da kuma yadda suke gudanar da sha'aninsu na sarauta,don haka ba zan iya zuwa wajensa ba saboda kada ajina ya zube".

Jakadiyarta dariya ta yi tana ganin wauta da kuma ƙuruciya ce ta ke damun Salimat don haka bata ƙara cewa komai ba ta fita daga ɗakin don tasan halin ƴaƴan sarauta akwaisu da kafiya.

Tun rana Aliyu ya dawo amman ko nan da cen baije ba,don yana shiga ɗakinsa da ya yi wanka yabi lafiyar gado ya ƙwanta don baya son hayaniya.

Rasheeda kuwa tana cen hankalinta a tashe don tana saka ran dawowar miji amman kuma taji shiru,don haka da kanta da daddare ta shirya cikin wasu arnan kayan bacci wanda sunansu sabon salon fanɗarinka a waje.

Sannan ta ɗakko wani turarenta wanda Hajiyar Aliyu tayo mata oder ɗinsa tun daga Sudan,matuƙar namiji ya shaƙesa to fa ya gama aiki.

A hankali ta fara ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin,shi kuwa Aliyu ya zata mai kawo mishi abinci ne ya ce"come in".

Babu wani jan aji Rasheeda ta shigo tana wani takunta kamar wata munafuka,tana shigowa ta cire hijabinta kai tsaye ta yi wajen Aliyu.





*Miss green ce*

Kuyi min afuwa rashin charge ne👏🏻

Na gama littafin darasi free page,don haka idan mutum yana da buƙata ya tintibeni ta wannan no ɗin.

Ga ɗanɗano da ga littafin darasi na payments.

DARASI!DARASI!!DARASI!!!

Alokacin General A.ya shigo da muƙarabansa waɗanda suka rakosa motoci sunfi goma sha,tun daga nesa ya ke kallon kyakkyawar halittar Fahima ga gashinta sai ɗagawa ya ke kamar wara ba indiya ko balarabiya,ya yi tsaye yana kallonta yana mamakin a ina aka samo wannan kyakkyawar yarinyar?.

Dai dai lokacin aka tsuge da ruwan sama mai tattare da ni'ima da ƙanshin ƙasa haɗi dana flowers ɗin gidan,ga wata iska mai daɗi.

Tsalle Fahima ta ke tana wasa da ruwan kana ganinta ka ga yarinya,a hankali Ammar ya biyo ta bayanta ya cire rigar sanyin da ya saka ta sojoji ya lulluɓawa Fahima,da sauri ta juyo cikin tsoro,aka yi rashin sa a ta zame ta faɗo ƙirjin Ammar yadda kasan awani indian film haka abin ya faru,daga shi sai singlet,gashin ƙirjinsa ya ƙwanta kamar wani gashin jariri.

Kallon ƙuda suka shiga yi babu ko ƙiftawa zuciyoyinsu sai bugawa suke kowannensu zai iya juyo ta ɗan uwansa.

A dai dai wannan lokacin kuma hancin motar Hajiya Sakinat ta shigo,bata kula da abin da ke faruwa ba sai da ta fito sai da ta da fa murfin motarta sannan ta iya tsayawa da ƙafafunta,idanunta sunyi jawur kamar gauta wata wutar jaraba da wutar kishi Sakinat taji a ƙirjinta,cikin wani irin mahaukacin sauri ta tunkaro inda su Ammar da Fahima suke.
_*🪁SILAR FYAƊE*🪁_

📃BOOK 2

UMMU MAHER(MISS GREEN🍀)

_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176  domin karin bayani,  maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka   fara amfani da   maganin zaki ga sauyi,  domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari  2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._

--------
*SIRRINKI👂🏻*

ƳAR UWATA ANASO BAYAN KIN GAMA AL'ADA KIDINGA TSARKI DA GANYEN MAGARYA,YANA CIRE INFECTION DA SAURAN ƘARNIN JINI👏🏻.

DAGA DR UMMU MAHER.
21🟪22

Yana kallon Rasheeda har ta shigo cikin kyakkyawan Ɗakin mijin na ta Babu ko gaisuwa ballantana sannu da zuwa ta ce"ashe ka dawo"?.

ta FaƊi hakan cikin yarensu na yoroba,banza ya yi mata ya tashi zaune sannan ya ce"kije ki kirawomin Salimat ku sameni a babban farlona".

yana faƊar hakan ya yi waje ko ajikinsa don duk wani iyayin da Rasheeda ta ke ko kallonta bai yi ba,ballantana ma yaga wata ƙwalliyar da ta yi mai.

Haushi da kuma dana sanin zuwanta ɗakin admiral A. Ya kama ta sai zagin kanta ta ke don sam arayuwarta ta tsani wulaƙanci tana matuƙar son admiral A. Shiyyasa ma ta ke shanye duk wani shariyarsa.

Sanda ta isa mangaren gimbiya Salimat wani ƙamshi mai mugun daɗi ya ziyarci hancinta,wani malulun baƙin ciki ya dirar mata,bata ƙara jin wani haushin ba sai da ta saka ƙafafunta a wani lallausan kafet mai mugun laushi ta haƊiye wani mugun yawu na baƘin ciki ta Ƙara sa shiga babban farlon wanda ya gaji da haɗuwa,duk kyan kayan Rasheeda sai taga na Salimat ya ta ka na ta a kyau da kuma tsaruwa komai na farlon white ne da kuma pink ya yi matuƙar yin ƙyau.

Tana cikin kallon farlon ne,jakadiya ta ce"baiwar Allah lafiya?baki iya sallama bane?"duk alokaci ɗaya jakadiya ta yi wannan tambayar.

Wani banzan kallo Rashida ta yi mata sannan ta ce"ki gayawa ita uwar mulkin maigidan yana son ganinta".

Da sauri Jakadiya ta ce"to bacci ta ke amman bari in tashi gimbiyar mata."tana faɗin hakan ta yi hanyar ɗakin Salimat.

"Ke dai ta ke gimbiyarki amman ni ba gimbiya ta ce ba".
Ado sosai Salimat ta yi da wata lifaya mai ƙyau fara ƙal sai ɗaukar ido ta ke,ta sha turaruka masu ƙamshi.

Sai da Rasheeda ta raina kanta ganin irin ƙwalliyar da Salimat ta yi.

Sallama ta yi sannan ta gaishesa,yaji daɗin gaisuwar da Salimat ta yi masa don ko babu komai ta girmama sa.

Rasheeda taji haushin abinda ya yi na amsa gaisuwar Salimat da ya yi ai kuwa ta cukule fuskarta tamau.

Abin yaso ya bawa Aliyu dariya amman sai ya basar da hakan,nasiha ya yi musu mai ratsa jiki sannan ya tabbatar musu da cewa Salimat ce uwargidansa tunda aurenta aka fara ɗaurawa.

Ai kuwa Rasheeda taji haushi sosai cikin yaran yoruba ta ce"gaskiya tun a yanzu ma nasan ba adalci za ayi ba".

ko kallonta baiyi ba don yasan abinda ta ce,sannan ya ce su tsara kwanakin da yafi yi musu,Rasheeda ta yi banza Salimat kuwa ta ce kwana biyu ya yi.

Tana faɗar hakan Rasheeda ta ce baiyi mata ba Aliyu ya ɗaga mata hannu sannan ya ce duk wacce ta nemi ta yar masa da hankali to fa zai yi displing ɗinta yadda ya kamata.

A take ta yi shiru don tasan waye Aliyu.

A ranar ya kamata Salimat ta amshi ƙwananta amman har dare ta rasa yadda za ayi taje wajensa don wata kunya da girman kai ta keji.

Kuyi haƙuri na yi typing kaɗan ayi manage.


*Miss green ce*
_*🪁SILAR FYAƊE*🪁_

📃BOOK 2

UMMU MAHER(MISS GREEN🍀)

Wattpad user name
   Rabiatu333

Arewabooks
rabiattu0444

---------
SIRRINKI👂🏻

ƳAR UWA KI KASANCE MAI RUFE SUTURARKI AKO DA YAUSHE,RUFE JIKINKI YANA TAIMAKA MIKI WAJEN YIN RIGAKAFI GA MUTANE DA KUMA SHAIƊANU.

   23🟩24

. . .. Har Ɗaki jakadiya Binta tabi Gimbiya Salimat don tasan tau ya kamata Salimat ta ƙwana a ɗakin mijinta Admiral A.tunda itace uwargidansa don aurenta aka fara ɗaurawa.

Tana zaune ta yi ta gumi ta sameta,Jakadiya ta samu waje ta zauna a ƙasa ta ce"uwar ɗakina idan babu damuwa aƙwai maganar da na ke so muyi da ke".
Salimat tasan maganar don haka bata ce komai ba ta tashi ta shiga bathroom Ɗin da ke manne ajikin Ƙaton ɗakin na ta,ɗan murmushi Jakadiya ta yi tana mamakin hali irin na Salimat kamar ba ita bace ta ke kukan son Aliyu ba,yanzu kuma ta sameshi sai ta yi wasarere dashi,ta yi wa mahaifiyar Salimat alƙawari tun kafin ta rasu za ta kula da Salimat kamar ita ta haifeta.
Kafin ta fito da sauri ta fita daga ɗakin taje ta ɗauko mata wani magani na sirri da ta aika aka kawo mata tun daga garinsu don ta yi dabarar sakawa Salimat a cikin madara don tasan ta da shan madara,shi wannan sirrin na dabanne wanda ke saka mace ta mallake mijinta ta hanyar shimfiɗarta.


***

babu abinda zance da zamana agidan ƙanwar mahaifiyata don babu abinda na nema na rasa,twins sun ƙara yin wani ƙyau da kuma ƙiba don suna samun abinci mai gina jiki,nima jikina ya ƙara ƙyau ni daman ya ya lafiyar kura don jikina jikin manyan mata ne na ƙara cika da ƙiba.

Ɗakina ma kaɗai abin kallo ne saboda yadda aka ƙawata shi gwanin sha'awa ga kuma suturu sai wanda na ke son zaɓa don wadrope ɗina cike ya ke da kaya masu ƙyau.

Rannan da yamma muna zaune a farlon Anty Rabi Layla ta ce"Sister don Allah inason ki rakani super marker in ɗanyo shopping".

ɗan murmushi na yi sannan na ce "babu komai Allah ya kaimu".

Idris ƙanin Layla ya ce"gaskiya ba za'aje da twins ba a barmin su muyi wasa."Dariya na yi na tashi na ce"ai ni daman yanzu na barmaka twins"dariya ya yi tayi yana murna wai na bar masa twins.

Ƴaƴan Anty Rabi huɗu ne uku maza mace ɗaya,maza biyun suna Germany acen suke karatu.
***
Ƙwalliya Salimat ta yi cikin wasu kayan bacci masu matuƙar ɗaukar hankali,sannan ta feshe jikinta da turaruka kala2,Sallama Jakadiya ta yi sannan ta ce"uwar ɗakina ga madara mai sanyi nasan kina so".

amsa Salimat ta yi tasha tana mai jin daɗin madarar,ta saka lifayarta mai ƙyau ta yi hanyar ɗakin oga Admiral A.

Ta saman bene Rasheeda ta hango Salimat za ta je ɓangaren mijinsu,wani irin malolon baƙin ciki ne ya ɗarsu a zuciyarta ta saka a zuciyarta matuƙar tana numfashi sai ta tarwatsa fadar Salimat,don ta yi alƙawarin sai ta wargaza fadar Salimat awajen Aliyu don ta lura tun yanzu fadarta mai yawa ce awajensa.



Kuyi haƙuri matsalar charge na ke da ita.

*Miss green ce*
_*🪁SILAR FYAƊE*🪁_

📃BOOK 2

UMMU MAHER(MISS GREEN🍀)

Wattpad user name
   Rabiatu333

Arewabooks
rabiattu0444

*addu'ar samun lfy ga ko wani irin ciwo*

an rawaito daga Aisha (R.A),tace manzon Allah(S.A.W)ya kasance idan mara lfy yazo wurinsa da kokena rashin lfy ya kan ɗauka hannunsa na tsakiya ya sanya a bakinsa sannan ya dangwali ƙasa sannan ya ɗaura a inda kewa mutumin ciwo,sai ya karanta wannan addu'ar kamar haka;

"bismillahir turbati ardina biriqati ba'dina yashfa Taqimuna bi'izni rabbina".

25/26

Da sallamarta ta shiga ɗakin hankalinsa na kan system ɗinsa ya ɗukufa da aiki ya amsa mata ya ɗan kalleta kaɗan sannan ya cigaba da aikinsa,waje ta samu aɗan kaɗan da nesa dashi ta ce"ina wuni"a hankali shima ya ce "lafiya"sannan ya kashe system ɗin ya ce mata yana zuwa.

Bai daɗe ba sai gashi ya shigo da wata ƙatuwar farar leda sannan ya ajje ya shiga bayinsa ya yi wanka da ɗaura alwala a inda ya barta anan ya dawo ya sameta ta sunkuyar da kanta ƙasa tana wasa da gefen mayafin lifayar ta ta,ya ce"tashi ki ɗauro alwala zamuyi sallah".a hankali ta tashi ta shiga banɗakin alwala tayo ta fito banɗakin nasa ya ƙawatu sosai wanda har sai da ya burge ta banɗakin kamar na mace komai fes dashi yana daga cikin abinda yasa ta ke matuƙar son Aliyu kenan aƙwai tsafta sosai.

Tana fitowa har ya tada sallah ta bishi suka yi har suka idar,a hankali ya ɗaga hannuwansa sama yana addu'ah tana amsawa da amin har suka gama tana jin ninkin ba ninkin ɗin son aliyu don bata Ƙara gasgata ilimin da ya ke dashi ba sai yanzu.

Ya kama goshinta ya shiga karanto mata addu'ar nan da manzon Allah(S.A.W) ya mana"alluhuma inni as'aluka khairaha wa khaira ma jabaltaha alaihi,wamin sharri ma jabaltaha washarri ma jabaltaha alaihi".

Kaza ce ƙatuwa mai girman gaske sai fresh milk ƙaton ƙwali uku mai sanyi sai shawarma wacce tun kafin a buɗeta ƙamshinta ya cika hancin mutum.

Tura mata kazar ya yi dukkanta sannan ya tsiyaya madarar yasha ya buɗe swan yasha sannan ya Ƙwanta ya ce"sai da safe".

wata ƙwallace ta biyo ta kuncin salimat ta kula kara kawai ya ke mata don kada ta fuskanci ba ya sonta,har cikin zuciyarta taji abin ya yi mata zafi amman yanzu ta wacce hanya ya kamata ta janyo hankalin aliyu don ya sota?babu mai bata amsa don haka ta Ƙwashe kayan ta kai fridge sannan ta Ƙudunduna a Ƙasan kafet ta Ƙwanta,aliyu yana kallonta sai da ya bari tayi bacci sannan ya sungumeta ya Ɗorata akan gadon sannan shi ya sakko Ƙasan ya Ƙwanta.



****

Da wuri na shirya na fito ina yiwa twins dariya don da sunga naci ado sai suyi ta maƘale min wai zamu tafi unguwa,yanzun ma haka ne ya faru suna hannun mama suka miƘomin hannu dariya mama ta yi sannan ta ce ai kuwz baza a tafi daku ba in rasa Ɗan hira".

ƴar dariya na yi sannan laila tace"ai kuwa ba zamu tafi dasu ba sun saka ayi ta ganin mamansu matar aure gwara mutafi siƘau Ɗin Mu".

har muka fito daga supet market na duba hannuna sannan na ce"ai kuwa laila na yi mantuwa"tsayawa ta yi a waje ni kuma na shiga don Ɗauko abinda na manta Ɗin wani anu naji na buge dashi kamar mutum don haka na juyo,,wata irin muguwar faƊuwar gaba naji tun daga kaina har Ƙasa na".

ina godiya sosai fans ɗina na darasi da sauran littattafaina ina godiya sosai akan nuna kulawar da kuka nuna min alokacin da na yi rashin lafiya,lol saƙo har yanzu sunyi min yawa,don Allah waɗanda ban duba nasu ba suyi min uzuri ina godiya.👏🏻🤝

*miss green*
_*🪁SILAR FYAƊE*🪁_

📃BOOK 2

*UMMU MAHER(MISS GREEN🍀)*

Wattpad user name
   Rabiatu333

Arewabooks
rabiattu0444

   27🟩28

Sosai gabana ya faɗi don ganin wanda na gani,bansanshi ba?ban san daga inda ya ke ba?amman kana ganinsa ba sai an faɗa maka ba matuƙar ka kalli twins ɗina zakaga babu abinda ya banbanta su kawai abinda ya banbantasu shi babba su kuma yara.

Kasa barin wajen na yi  shi kuwa yana ta siyayyarsa ya fito ta hanyar da na ke,wani glass ne na ɗora hannuna akai ban sani ba ina kallonsa kawai sai naji ya faɗi ƙasa ya tarwatse baki ɗaya,nan ta ke hankalin kowa yayo kaina,nima cikin tsoron na kalli glass ɗin.

Aliyu ma kallo inda yaji ƙarar glass ɗin ya yi sojoji biyu ne a tare dashi,kallona ya shigayi sosai ammanfa bani ɗin ya ke kallo ba hannuna ya ke kallo wanda ya yanke har yana fidda jini amman ni ban san yana fidda jinin ba saboda tsoro da firgici.

A hankali yazo inda na ke nima a lokacin kallon nasa na ke kawai don har yanzu mamakin kamannin na ke.

"Baiwar Allah kina bleeding baki sani ba".da sauri na kalli hannun wanda sai a yanzu naji zafin hannun,alokacin securities ɗin wajen sunzo suna ƙwashe glass ɗin da ya fashe.

Alokacin Layla ta shigo hankalinta a tashe tayo kaina don ganin hannuna yana fidda jini tana tambaya ta me ya faru?amman ban ba ta amsa ba baki na yana rawa na ke nuna mata Aliyu,kallon inda hannuna yabi ta ke yi,a ta ke itama tayo waje da idanuwanta tana kallon inda na ke kallo.

Aliyu mamaki ne ya kamashi ganin suna ta nuna sa alhali basu sanshi ba,ganin shima mamakin ya ke yasa Layla ta buɗe wayarsa ta tako a hankali wajen Aliyu ta buɗe mishi hoton twins.

Shima waro idanu waje ya yi ganin waɗannan yaran masu mugun kama dashi ya yi imanin cewa ko da ƴaƴansa ne da ƙer zasu yi irin wannan kamar.
Da sauri ya ce"baiwar Allah wannan yaran yaranki ne?".

A hankali Layla ta juya ta kalli Rabiatu sanman ta nuna ta da ɗan yatsa,kallon Rabiatu ya yi sosai ganin wai wannan ƴar yarinyar ce mahaifiyar yaran wacce ko a fuskarta bata nuna alamar ta taɓa haihuwa ba a ƙiyasce ma bata fi shekara 18 ba.

A hankali Aliyu ya ta ka ya i'sa wajen da Rabiatu ta ke wacce har a lokacin kallon Aliyu ta ke,a hankali ya ce "baiwar Allah biyo ni waje muɗanyi magana".

Cikin wata iriyar muryar da Rabiatu bata san tana da ita ba tace"in biyo ka kace fa?ka ɗauka zaka ƙara yaudarata yadda ka yaudareni a baya,ka lalata min rayuwata ka cutar dani da gurɓatattun ƴaƴan da ka yi min fyaɗe na haifa maka".

da sauri Aliyu ya juyo jin furucinta fuskarsa ta yi wani irin jajir jijiyoyin kansa suka tashi,da alamar allurar nan ta sojoji za ta tashi,da wani irin sauri ya fita don barin wajen don gani ya ke kamar a mafarki wai yau wata ce ta ke ce masa wai ya yiwa mata ciki.

Da sauri Layla ta kamo hannun Rabiatu don subar wajen don har mutane sun fara taruwa.

Muna fitowa muka iskesa a waje na ta ka a hankali naje inda ya ke,kallonsa na ke gabana yana mugun faɗuwa don ba ko wacce mace ce zata iya kallon Aliyu ta yi masa furucin da na yi masa ba na ce"Bawan Allah idan har kana ja inja akan ba kaine uban waɗannan yaran dana haifa ba muje ayi gwaji hakan shine zai ƙara tabbatar min da zargina don wallahi ko rantsuwa bana yi kaine uban twins.

Da sauri Ola wato sojan dake hannun daman Aliyu zai dakatar dani akan maganar da na kewa ogansu,shima Aliyu da sauri ya ɗaga hannu ya dakatar dashi don ko babu komai wannan yarinyar macece.

Aliyu baice komai ba ya ce"bayin Allah muje asibiti sannan ku ɗauko yaran?don gaskiya ni nasan ban taɓa auren wacce mace na saki ba,ballan tana ace ma wai harni Aliyu inyiwa wacce mace ciki amman ni nasan Allah yana nan.

Motar Aliyu daban tasu Haidar wato Aliyu daban.

Sai da suka shigo layin sannan yaga ashe layin da ya ke ne amman bai ce komai ba.

Atare suka fito harda Mama da kuma su Twins,Mama ma mamaki sosai ta ke na ganin Aliyu don babu abinda zaisa kaƙi cewa shine babansu Twins,shima Aliyu sai yanzu ya ke ganin wata muguwar kamar da sukayi da yaran kallonsu kawai ya ke yana kabbara har a fili.

Wani private hospital suka je aka yi sa a suna zuwa suka shigar da ƙorafinsu aka ɗauki jininsu dukka,shi kuwa Aliyu mamaki kawai ya ke wai yau shine a asibiti ana gwada jininsa wai ana zarginsa da yiwa mace ciki.

Suna zaune wata nurse ta fito ta ce"wai ku shigo dukkanku.

Suna shiga kowa hankalinsa yana kan takaddar gabansa yana faɗuwa,shi kansa likitan sai da gabansa ya faɗi ganin ƴan biyu da kuma Aliyi don kamannin har sunyi yawa.

A hankali ya fara faɗar sakamakon kamar haka;

"a gaskiya wannan gwajin da aka yi ya tabbatar da ƙwatata jinin wannan yaran dana wannan  bawan Allah ƙwata2 ba shine mahaifinsu ba. ..... .

Da wani irin ihu Rabiatu ta yi sannan ta sume a ƙasa sumammiya.


*Tirrrrrƙashi*

anan zan tsaya a wannan littafin na wa mai suna Silar fyaɗe  sai a littafi na gaba wato book3 zamuji tarin tambayoyinku akan waye mahaifinsu twins?bayan ALIYU wa kuke zargi shine nahaifinsu twins?.

kuyi haƙuri Fans wannan litrafin banyo niyyar mayar dashi na kuɗi ba ,saboda wasu abubuwa da suka faru yasa zan mayar dashi kuyi haƙuri👏🏻.

Naira 200kacal ban tsaurara ba ko katin mtn ko ta acc.

Ga masu neman ƙarin bayani ku nemeni ta wannan number tawa.

07068606171
Ummu maher ce👏🏻

No comments